Moise ya lashe zaben Haiti
Hukumar Zaben Haiti ta ce Dan Kasuwa Jovenel Moise da ke samun goyan bayan tsohon shugaban kasa Michel Martelly ya lashe zaben kasar da kuri’u sama da kashi 55.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Jami’in gudanar da zaben Uder Antoine ya ce Moise ya doke Jude Celestin na Jam’iyyar LAPEH da ya zo na biyu da kashi kusan 20, yayin da Moise Jean Charles ya zo na uku da kasha 11.
Dokar kasar ta bai wa dan takarar da bai gamsu da sakamakon ba ya ruga kotu domin kalubalantar sakamakon.
Moise dan kasuwa mai shekaru 48 bai taba rike wani mukamin gwamnati ba, amma ya sha alwashin habaka kasar.
‘Yan takara 27 suka fafata a zaben inda hudu daga cikinsu suka yi gaggawar sanar da samun nasara a zagayen farko kafin sanar da sakamakon a hukumance.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu