Isa ga babban shafi
Britaniya-Amurka-Najeriya

Birtaniya da Amurka sun bankado shirin Boko Haram na Sace 'yan Kasashen Waje dake Najeriya

Kasar Birtaniya da Amurka sun sanar da gano yunkurin kungiyar Boko Haram na  fara satan baki ‘yan kasashen waje suna garkuwa da su a yankunan Arewa maso gabashin Najeriya.

Wasu sojan Najeriya dake sintiri a Maiduguri don gano mayakan Boko Haram
Wasu sojan Najeriya dake sintiri a Maiduguri don gano mayakan Boko Haram Photo: Stefan Heunis
Talla

A cewar ofishin kula da harkokin waje na London, sun sami wasu gamsassun bayanai dake nuna ‘yan kungiyar Boko Haram na shirin sace ‘yan kasashen waje dake karamar Hukumar Bama na jihar Borno dake kusa da kasar Kamaru.

Ofishin jakadancin Amurka dake Abuja  ya bayyana cewa Amurkawa dake wannan yanki su yi hattara.

‘Yan wannan kungiya ta Boko Haram  sun sha sace mutane da suka hada da mata da yara kanana daga wannan yanki.
 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.