Shugaban Faransa Macron na Ziyara a Mali Yau
Shugaban Faransa Emmanuel Macron na ziyara a kasar Mali yau Lahadi a kokarin da kasar sa ke yi don marawa kasashe biyar na yankin Sahel baya su yaki masu ikirarin jihadi da 'yan ta'adda a yankunan.
Wallafawa ranar:
Kasashen biyar da suka hada da Nijar, Burkina Faso, Mali, Chadi da Mauritania sun lashi takobin kawar da masu ayyukan ta’addanci da masu jihadi dake yankin kasashen su, kuma kasar Faransa ta bayyana bada nata gudun mawa.
Emmanuel Macros zai shiga taron shugabannin kasashen biyar da za su yi a Bamako inda zai bayyana irin gudunmawar da za su samu.
Dakarun hadin guiwa na kasashen biyar mai cibiya a garin Sevare dake tsakiyar Mali na da Dakaru dubu biyar don shiga sauran Dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya su dubu sha biyu da suka hada da na Faransa dubu hudu dake yankin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu