Isa ga babban shafi
Haiti

Girgizar kasa ta kashe mutane 11 a Haiti

An sami girgizan kasa mai karfi a Haiti wadda ta kai maki 5.9 a ma’auninta inda ta kashe mutane akalla 11 da lalata gidaje masu yawan gaske.

Mutane sun rasa muhalli a yayin girgizan kasa da aka samu a Haiti a shekara 2013
Mutane sun rasa muhalli a yayin girgizan kasa da aka samu a Haiti a shekara 2013 rfi
Talla

Kakakin Gwamnatin kasar Eddy Jackson Alexis ya fadawa manema labarai cewa cikin mamatan guda bakwai sun mutu ne a garin Port-de-Paix yayin da mutane hudu sun gamu da ajalinsu ne a garin Gros-Morne mai tazaran kilomita 50 ta shiyyar kudu maso gabashin kasar.

Kamar yadda Hukumar dake Kula da harkokin jama’a ta sanar akwai mutane 135 da suka jikkata.

Girgizan kasar ta yi barna a garuruwan Chansolme da tsubirin Tortuga.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.