Isa ga babban shafi
UNICEF

UNICEF za ta tallafawa yara miliyan 39 da yaki ya daidaita a gabas ta tsakiya

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya ya kaddamar da gidauniyar neman dala miliyan 2 da rabi don tallafawa yara miliyan 39 a gabas ta tsakiya, wadanda radadin yake-yake, talauci da annobar coronavirus ya shafa.

Wasu kananun yara da ke rayuwar kunci a Yemen.
Wasu kananun yara da ke rayuwar kunci a Yemen. REUTERS/Ali Owidha
Talla

Babban Daraktan UNICEF a yankin gabas ta tsakiya Ted Chaiban, ya ce yankin na kunshe da yara kanana da ke cikin yanayi na matukar bukata, wanda ya ce sun hada da tasirin radadin yake-yake, talauci da koma-bayan tattalin arziki.

Ya ce asusun ya mika bukatar baya-bayan nan ne don tallafawa yaran da ke cikin matsanancin bukatar jinkai, kuma ke ci gab da samun matsaloli sakamakon bullar annobar COVID 19.

A wata sanarwar asusun na UNICEF ya ce yara na cikin matsanci bukata a yankunan da yaki ya daidaita a Yemen da Syria da Sudan, inda a Yemen yara miliyan 12, ko kuma ma kowane yaro yake neman agaji biyo bayan yakin da aka shafe shekaru 5 ana yi.

A Syria, kusan yara miliyan 5 ne ke bukatar a agaza musu bayan yakin basas aya lakume rayuka sama da dubu dari 3 da 80, ya kuma jefa kasar a cikin matsain tattalin arziki.

A Sudan, yara miliyan 5 da dubu dari 3 na bukatar kama musu, bayan da ambaliyar ruwa da ba taba ganin irinta ba, da kuma matsalar tattalin arziki suka addabi kasar.

A Lebanon kuwa, yara miliyan 1 da dubu dari 9 ne ke dogaro da taimako,biyo bayan fashewar wani abu da ta kashe mutane fiye da 200 ta kuma lalata wasu sassan babban birnin kasar, Beirut a watan Agusta.

Sanarwar ta jaddada cewa ba zai kyautu duniya ta yi gum tana kallon yara cikin matsanancin bukata ba, sakamakon munanan yake yake 2 a tarihi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.