Amurka ta nemi kawayenta su kwashe jama'arsu daga Syria don murkushe IS
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya kara matsin lamba ga kasashe aminan kasar kan su fara aikin kwashe jama'arsu da aynzu haka ke tsare a Syria a wani yunkuri na hanasu shiga kungiyar ta'addanci ta IS, ya na mai gargadin cewa ba za a ci gaba da rike su a Syria na har abada ba.
Wallafawa ranar:
Blinken ya yi wannan kiran ne yayin ganawa da kawancen kasashen mambobi 83 na kawo karshen kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi a duniya, a wani taro da suka gudanar a birnin Rome na kasar Italiya, inda suka yi kira da a mai da hankali sosai ga barazanar mayaka masu ikirarin jihadi a Afirka.
Wani kiyasin Amurka ya nuna akwai mayakan IS kimanin dubu 10 da suka fito daga kasashe daban-daban dake tsare a hannun mayakan Kurdawa dake taimakawa kawancen kasashen yamma a arewacin Syria.
Blinkin ya ce, "Amurka na ci gaba da kira ga kasashe – masamman na kawancen - da su dawo da su gida, domin gyara musu hali, ko gurfanar da wadanda suka cancanci hukunci.
Faransa da Birtaniya dake matsayin manyan aminan Amurka, na yin dari-dari dangane da kiraye-kirayen dawo da ‘yan kasarsu gida, wanda tun gwamnatin tsohon shugaban kasar Donald Trump ta yi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu