Isa ga babban shafi
Haiti

Mai dakin marigayi shugaban Haiti ta yi magana a karon farko

Mai dakin shugaban kasar Haiti da aka raunata a harin da ya lakume ran mijinta Jovenel Moise ta yi magana a karon farko a ranar Asabar tun bayan mummunar raunin da ta ji, inda ta yi kira ga al’ummar kasar  da kada su karaya.

Marigayi shugaba Jovenel Moise na Haiti tare da mai dakinsa Martine Moise.
Marigayi shugaba Jovenel Moise na Haiti tare da mai dakinsa Martine Moise. HECTOR RETAMAL, HECTOR RETAMAL AFP/Archivos
Talla

A wani sakon murya da aka wallafa ashafinta na Twitter, Martine Moise ta bayyana godiya ga Allah da ya yi mata tsawon kwana, kwanaki 3 bayan da wasu suka harbe mijinta har lahira a gidansa.

Ministan yada labarai da al’adu na kasar Pradel Henriquez ya tabbatar wa da kamfanin dillancin labaran Faransa sahihancin sakon.

Hukumomin Haiti sun ce wata tawagar mahara mai mutane 28 ne suka fasa gidan shugaban kasar suka aika da shi  lahira.

Ya zuwa yanzu an kama 17 daga cikinsu, aka kuma kashe akalla 3, yayin da ake ci gaba da farautar sauran.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.