Isa ga babban shafi

Za’a dawo da hukuncin yanke hannu a Afghanistan

Kungiyar Taliban, ta bayyana cewa, za’a dawo da zartas da yanke hukuncin yanke hannu, da na kisa ga wanda suka aikata laifin da ya kai a yanke musu hukuncin a Afghanistan.

Yan kungiyar  Taliban
Yan kungiyar Taliban Bulent KILIC AFP
Talla

Shugaban hukumar gidajen yari na kungiyar Taliban, Mullah Nooruddin Turabi, ya shaidawa manema labarai cewa, wannan hukunci ya zama wajibi don tabbatar da tsaro.

Ya ce, ba za’a dinga aiwatar da shi a bainar jama’a ba, ba kamar yadda ya gudana a tsohon mulkin Taliban a cikin shekarar alif 990 ba.

Matan taliban
Matan taliban AP - Rahmat Gul

Tin lokacin da Taliban ta kwace mulkin a 15 ga watan Agustan shekarar da muke ciki ne ta yi alkawarin gudanar da mulki, ba tsangwama, ba kamar yadda suka yi a tsohon mulkin su ba.

Amma a halin yanzu, ana ta samun rahotannin da suka shafi tauye hakkin bil’adaman da ‘yan kungiyar ke yi a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.