Isa ga babban shafi

Idan aka kaiwa Belarus farmaki za mu bi sahun Rasha - Lukashenko

Shugaba Alexander Lukashenko na Belarus y ace kasar a shirye take ta yi yaki tare da babbar kawarta Rasha a Ukraine idan aka kai wa kasarsa hari.

Shugaban Rasha Vladimir Putin kenan yayin da yake musabaha da takwaransa na Belarus Alexander Lukashenko yayin wani taro Sochi, da ke kasar rasha ranar 26 ga watan satumban 2022.
Shugaban Rasha Vladimir Putin kenan yayin da yake musabaha da takwaransa na Belarus Alexander Lukashenko yayin wani taro Sochi, da ke kasar rasha ranar 26 ga watan satumban 2022. via REUTERS - SPUTNIK
Talla

"A shirye nake da na marawa Rasha baya daga Belarus ba tare da bata lokaci ba: Idan ko da soja daya ya zo cikin yankin Belarus don ya kashe mutanena," shakka babu zan hada kai da Rasha wajen daukar fansa,” in ji Lukashenko a wani taron manema labarai.

Ya kara da cewa "Idan suka yi ta'addanci a kan Belarus, martani zai kasance mafi tsanani, kuma yakin zai dauki salo daban-daban."

Sojojin Rasha sun yi amfani da yankin Belarus a matsayin wurin kaddamar da farmakin da aka kai wa Ukraine a watan Fabrairun da ya gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.