Isa ga babban shafi
RIKICIN ISRA'ILA DA HAMAS

Isra'ila ta sake aukawa kudancin Gaza da luguden wuta

Luguden wutar da Isra’ila ke yi a birnin Rafah na kudancin Zirin Gaza ya shafi gidaje, al’amarin da ke ta’azzara abin da kungiyoyin  agaji suka bayyana a matsayin mummunan yanayi, duk kuwa da kokarin da ake na cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.

Yadda harin Isra'ila ya lalata sansanin 'yan gudun hijira na Rafah da ke kudancin Gaza.
Yadda harin Isra'ila ya lalata sansanin 'yan gudun hijira na Rafah da ke kudancin Gaza. AFP - MOHAMMED ABED
Talla

Barin wutar da Isra’ilar ke yi  ya lalata wani gida, kana ya huda wani katafaren rami a gabashin birnin Rafah, inda akalla al’ummar Gaza su kimanin miliyan 1 da dubu dari 4 ke neman mafaka daga rikicin da ake yi.

Wannan yaki ya barke ne bayan da mayakan Hamas  suka kai wani hari cikin Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoban shekarar da ta gabata, lamarin da ya yi  sanadin sama da mutane dubu daya.

A asibitin Najjar da ke kudancin birnin Rafah , masu zaman makoki sun rungume gawarwakin wasu kananan yara da aka rufe fuskokinsu da farin kyalle.

Bayanai sun ce, an yi luguden wuta a gundumar Zeitun da ke makwabtaka da Rafah, inda aka jibge tankokin yaki, da sojoji.

Sojojin sun ce jirage masu saukar ungulu na ci gaba da taimakawa ‘dakarun da aka tura yankin, domin yakar Hamas.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.