Isa ga babban shafi

Dubban mutane sun yi zanga-zangar kin jinin Isra'ila a sassan duniya

Dubban mutane sun bazama kan tituna a sassan duniya musamman a kasashen yankin Gabas ta Tsakiya, domin nuna goyon bayansu ga Falasdinawa, a daidai lokacin da Isra'ila ke shirin kaddamar da farmaki ta kasa kan Zirin Gaza.

Dubun dubatar 'yan kasar Jordan a birnin Amman, yayin zanga-zangar baya ga Falasdinawa a Gaza, 13 ga Oktoba, 2023.
Dubun dubatar 'yan kasar Jordan a birnin Amman, yayin zanga-zangar baya ga Falasdinawa a Gaza, 13 ga Oktoba, 2023. REUTERS - ALAA AL SUKHNI
Talla

Masu zanga-zangar sun yi ta yin tir da harin bama-bamai ta sama da Isra’ila ke kai wa kan yankin na Gaza babu kakkautawa, inda ya zuwa yanzu sama da mutane dubu 1 da 900 suka mutu, matakin da ta ce martani ne kan farmakin ba-zatar da mayakan Hamas suka kaddamar kanta, tare da kashe mata mutane fiye da 1 da 300.

A Bagadaza babban birnin kasar Iraqi, dandalin taro na Tahrir jama'a suka cika domin amsa kiran jagoran mabiya Shi'a Muqtada al-Sadr don yin Allah wadai da Isra’ila.

A Sanaa kuwa, babban birnin Yemen da kuma kasar Jordan, masu zanga-zangar da suka fita kan tituna, daga tutocin kasashen suka rika yi da na Falasdinawa.

Mabiya fitacccen malami Moqtada al-Sadr a Iraqi yayin addu'o'i ga Falasdinawa a Zirin Gaza.
Mabiya fitacccen malami Moqtada al-Sadr a Iraqi yayin addu'o'i ga Falasdinawa a Zirin Gaza. REUTERS - SABA KAREEM

A birnin Islamabad na Pakistan, taka tutocin Amurka da na Isra’ila masu zanga-zanga suka rika yi gami da yin Alla wadai da su.

A Kuala Lumpur babban birnin kasar Malaysia, kimanin Musulmai dubu 1 ne suka gudanar da zanga-zanga tare da kona tutocin Isra'ila.

Malaman addinin Musulunci a Indonesia kuwa, kira suka yi ga dukkanin masallatan kasar da su gudanar da addu’o’i na musamman don nemawa  Falasdinawa tsaro da  zaman lafiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.