Isa ga babban shafi
FIFA

Harambee Stars na iya ba Super Eagles mamaki, inji Wanyama

Victor Wanyama Dan wasan kungiyar Celtic a Birtaniya ya ce Kenya na iya doke Najeriya a gobe Assabar wadanda za su kara a birnin Calabar a wasa neman shiga gasar cin kofin Duniya da a’a gudanar a Brazil a shekarar 2014.

Dan wasan Kenya Victor Mugubi Wanyama yana fafatawa da dan wasan Togo Salifou Mustapha a wasannin neman shiga gasar cin kofin Afrika
Dan wasan Kenya Victor Mugubi Wanyama yana fafatawa da dan wasan Togo Salifou Mustapha a wasannin neman shiga gasar cin kofin Afrika Reuters/Noor Khamis
Talla

‘Yan wasan Super Eagles na Najeriya suna da damar doke ‘yan wasan Harambee Stars na Kenya saboda dubban ‘yan kasar da za su shiga filin wasa domin mara masu baya.

Najeriya ce dai ke jagorancin rukuninsu da maki 4 bayan ta doke Namibia da ke a matsayi na biyu da maki 3. Kenya kuma tana matsayi na karshe ne kasan Malawi da zata kara da Namibia.

A birnin Ouagadougou kuma Burkina faso za ta karbi bakuncin Jamhuriyar Nijar
Congo kuma da ke jagorancin teburin rukuninsu da maki 6 za ta kai wa Gabon ziyaara ne wacce aka ragewa maki saboda ta yi amfani da dan wasan da be dace ba.

‘Yan wasan Eagles na Mali kuma za su kara ne da Rwanda yayin da kuma Sudan ta kece raini da Ghana.

A baya dai an datsewa Sudan yawan maki 3 saboda ta yi amfani da dan wasan da be dace ba a wasanta da Zambia. Kuma yanzu Zambia ce ke jagorancin Teburinsu na H da tazarar maki 6 tsakaninta da Ghana.

‘Yan wasan Elephant na Cote d’Voire kuma zasu kara ne da Gambia

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.