An soke zaben yankin Zanzibar na kasar Tanzania
A kasar Tanzania al’umma sun soma bayyana shakkunsu dangane da sahihancin zaben kasar da ake jiran bayyana sakamakonsa a gobe alhamis, wannan dai ya biyo bayan soke zaben yankin tsibirin Zanzibar.
Wallafawa ranar:
Shugaban Hukumar zabe na tsibirin Zanzibar Jesha Salim Jesha ya bukaci sake gudanar da zaben bayan zargin cewa akwai kurakurai da suka sabawa dokoki abinda yasa yace ya zama dole a soke zaben.
Wannan al’amarin na iya kawo jinkiri wajen bayyana sakamakon babban zaben kasar da al’umma ke dakon jin sakamakon a gobe .
Akalla mutane dubu dari biyar ne suka yi zabe a tsibirin Zanzibar
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu