Isa ga babban shafi
Najeriya

An samu gawar hafsan sojin da aka sace a Najeriya

Rundunar Sojin Najeriya ce ta sanar da labarin samun gawar kanar Samaila Inusa hafsan sojin nan da aka sace a karshen mako a yau talata da misalin karfe 6 na yamma.

Janar Tukur Buratai, babban hafsan sojin Najeriya
Janar Tukur Buratai, babban hafsan sojin Najeriya AFP PHOTO/STRINGER
Talla

Sanarwar da rundunar sojan ta bayar ta hannun Daraktan yada labaran ta Kanar Sani Usman Kukasheka tace ana kyautata zaton an kashe hafsan ne ranar da aka sace shi, domin har gawarsa ta  soma lalacewa.

Rundunar tace an samu gawar ce kusa da kauyen Ajyaita dake wajen jahar Kaduna.

Daraktan ya bayyana cewar rundunar sojin ba za tayi kasa a gwiwa ba wajen zakulo wadanda suka kashe hafsan dan hukunta su.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.