Isa ga babban shafi
Najeriya

Majalisar Dattawan Najeriya ta Gayyaci Ministan Sharia Abubakar Malami

Wakilan Majalisar Dattijan Najeriya sun umarci Ministan Sharia kuma Atoni Janar na kasar Abubakar Malami  ya gurfana gaban Majalisar don yin bayani gameda zargin da ake yiwa Shugaban Majalisar Dattijan da Mataimakin sa na laifin sauya dokokin majalisa.

Bukola Saraki na rantsuwar kama aiki a matsayin Shugaban  Majalisa na 8 a Najeriya.
Bukola Saraki na rantsuwar kama aiki a matsayin Shugaban Majalisa na 8 a Najeriya. REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Gayyatar Ministan na biyo bayan bukatar hakan ne daga Dan Majalisa Dino Melaye wanda yake cewa akwai matsala da ya hango dake neman yiwa tsarin Democradiyya lahani.

Wakilan majalisar Dattijai shida suka tofa albarkacin bakin su suna nuna goyon bayan su gameda bukatar gayyato Ministan Sharia yayi bayani.

Gwamnati na zargin Shugaban majalisar ne Bukola Saraki da mataimakin sa Ekweremadu da laifin sauya kundin tafiyar da harkokin majalisar don zaben da aka yi masu na Shugaba da mataimakin shugaban majalisa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.