Najeriya
Tsagerun Niger Delta zasu gana da Gwamnatin Najeriya
Kungiyar Tsagerun Naija Delta da ake kira Niger Delta Avengers tace a shirye take ta tattauna da gwamnatin Najeriya don kawo karshen tashin hankalin da ake samu a yankin.
Wallafawa ranar:
Talla
Mai Magana da yawun kungiyar Ballantryre Agiri ya shaidawa manema labarai cewa sun kafa kwamitin da zai wakilce su a tattaunawar, kuma suna da yakinin cimma matsayar da zata kai ga samun zaman lafiya a yankin.
Sai dai wasu Yan Najeriya na kallon sanarwar a matsayin yaudara, kamar yadda suka ce ansha jin irin wannan alkawari daga bangaren tsagerun.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu