Isa ga babban shafi
Najeriya

"Za'a kammala gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya a sabuwar shekara"

Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Bukola Saraki, ya ce Majalisar zata kammala gyaran kundin tsarin mulkin kasar cikin watan Janairu na sabuwar shekara.

Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya kuma tsohon Gwamnan Jihar Kwara Bukola Saraki
Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya kuma tsohon Gwamnan Jihar Kwara Bukola Saraki REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Saraki ya sanar da haka ne, yayin karbar bakuncin shugaban Kungiyar Lauyoyi ta kasa Abubakar Mahmud (SAN).

Shugaban Majalisar Dattawan ya ce kwaskwarimar kundin tsarin mulkin, ta bawa sashin gyaran fuskar dokokin gudanar da zabukan Najeriya muhimmanci, da suka kunshi, batun dage zabuka bisa dalilan tsaro da kuma inganta tsarin gudanar da kada kuri’a a lokutan zabe.

Karin wasu daga cikin sauran fannonin da za'a yiwa gyara sun hadar da dokokin tafiyar da sashin Shari’ar Najeriya, Ma’aikatar kula da gidajen Yari, da kuma, dokokin tafiyar da hukumomin, yaki da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC, da kuma ta yaki da cin hanci da rashawa, ICPC.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.