Majalisar Najeriya za ta kai karar NNPC a gaban EFCC
Kwamitin Majalisar Walikan Najeriya da ke nazari kan farashin albarkatun man fetir ya yi barazanar shigar da karar jami’an kamfanin mai na NNPC a gaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa wato EFCC sakamakon zargin su da hannu a wata badakalar kudaden ketare.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Wannan na zuwa ne a yayin da wasu kamfanonin mai suka musanta karban kudaden duk da cewa babban bankin kasar CBN ya ce sun karba kudaden don gudanar da aikin mai a kasar.
Shugaban Kwamitin Raphael Nnanna Igbokwe ya ce, za su yi bincike mai zurfi don gano yadda badakalar ta rufa-rufa ta shafi jami’an NNPC.
A makon jiya ne hukumar EFCC ta cafke wasu darektocin CBN saboda zargin su da hannu a badakalar bada kudaden na ketare.
Tuni dai kwamitin ya bukaci karamin Ministan Mai na Najeriya Dr, Ibe Kachikwu da Gwamnan babban bankin kasar Godwin Emefiele da su bayyana a gabansa a ranar Jumma’a mai zuwa don bada cikakkun bayanai kan wannan lamari mai sarkakiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu