Isa ga babban shafi
Najeriya

Rundunar 'Yan sandan Najeriya ta nemi hadin kan Sarakuna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce har yanzu tana dakon amincewar shugaban kasar Muhd Buhari, kan bukatar da ta gabatar masa, dangane da daukar sabbin jami’an ‘yan sanda 30,000 duk shekara har tsawon shekaru 5.

Nigeria Police
Nigeria Police Photo: Reuters
Talla

Maigari Abbas Dikko, mataimakin babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya mai kula da samarwa da kuma kayan aikin rundunar ne ya sanar da hakan a lokacin da ya ziyarci gwamnan jihar Kebbi Abubakar Atiku Bagudu.

Dikko ya bukaci hadin sarakunan gargajiya da gwamnoni wajen tantance sabbin jami’an ‘yan sandan da za’a dauka da zarar shugaba Buhari ya amince da bukatar.

A cewar mataimakin sifeto janar Dikko, a halin da ake ciki, yawan jami’an ‘yan sandan Najeriya bai zarta 380,000 ba, lamarin da ya sa tilas a dauki karin 155,000 cikin shekaru biyar. domin cika ka’idar da majalisar dinkin duniya ta ware kan aikin dan sanda.

Karkashin ka'idar dai kamata yayi duk jami'in dan sanda guda ya kula da mutane akalla 400.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.