Makaman 'Yan Sandan Najeriya sun yi batan-dabo
Wani rahoton bincike ya nuna cewa, akalla makamai mabanbanta har guda 44 mallakar rundunar ‘yan sandan Najeriya sun yi batar-dabo tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Lamarin dai ya haifar da fargabar yiwuwar cewa, makaman sun fada hannun wasu miyagu da suka hada da 'yan fashi da makami da kuma masu garkuwa da jama’a don karbar kudin fansa.
Ofishin babban mai binciken baitil-malin gwamnatin tarayya ne ya gudanar da bincieken kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya ba shi dama.
Tuni dai masharhanta kan sha’anin tsaro suka fara tofa albarkcin bakinsu game da rahoton.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu