Boko Haram: Ouattara ya jijinawa Buhari
Shugaban Kasar Cote d’Ivoire Alassane Ouattara ya bayyana gamsuwa da rawar da Najeriya ke takawa wajen yaki da kungiyar Boko Haram
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
A ziyarar da ya kawo Najeriya, Ouattara ya yaba da shugabancin da kasar ke samarwa a fadin Afirka baki daya.
Shugaba Muhammadu Buhari da ya shafe tsawon lokaci yana tattaunawar sirri da Ouattara, batutuwan tsaro da tattalin arziki sune muhimman abubuwan da suka mayar da hankali akai.
Kana shugabanni biyu sun kuma tatattauna rikicin Togo da halin da ake ciki a Liberia, kazalika taron Kungiyar Tarayyar Afirka da EU da za a gudanar a watan Gobe a Abidja.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu