Isa ga babban shafi
Najeriya

Babu rabuwa tsakanin kabilar Ibo da Najeriya - Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya bukaci al’ummar kasar na yankin kudu maso gabashi, su yi watsi da farfagandar ‘yan neman tada zaune tsaye, masu neman ballewa daga kasar.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, sanye da hular sarautar gargajiya da, sarakunan kabilar Ibo suka bashi, yayinda ya ziyarci jihar Ebonyi, ranar 14 ga Nuwamba, 2017.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, sanye da hular sarautar gargajiya da, sarakunan kabilar Ibo suka bashi, yayinda ya ziyarci jihar Ebonyi, ranar 14 ga Nuwamba, 2017. RFIHAUSA
Talla

Buhari yayi kiran ne, a garin Abakaliki, a lokacin jawabi ga taron jama’ar garin, yayinda ya ziyarci jihar Ebonyi a ranar Talata.

Shugaban babu rabuwa tsakanin kabilar Ibo da Najeriya, kan haka ne kuma ya ziyarce su, don tabbatar zaman Najeriya a dunkule. Zalika ya kuma tabbatar musu da cewa gwamnatinsa zata cika alkawuran da ta dauka na aiwatar da manyan ayyuka a yankin.

A lokacin ziyarar ce kuma sarakunan gargajiya na Kabilar Ibo, a karkashin jagorancin Eze Eberechi Dick, suka karrama Buhari, da mukamin sarautar gargajiya ta Ochioha Ndigbo wato (jagora ga ‘yan kabilar Ibo).

A baya wani bangare na kabilar ta Ibo, ya sha kokawa da nuna adawa ga gwamnatin Muhammadu Buhari, bisa zargin baya damawa da ‘yan kabilar cikin harkokin kasa, lamarin da ya kai ga kungiyar IPOB karkashin jagorancin Nnamdi Kanu karfafa aniyar da ta dade da kudurewa ta ballewa daga Najeriya. Sai dai an kwantar da tashin hankalin da nemi barkewa, bayan matakan da hukumomin tsaron kasar suka dauka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.