Najeriya ta kwaso bakin-haure 1, 295 daga Libya cikin Nuwamba
Wani kashi na bakin-haure ‘yan Najeriya da suka makale a Libya, da yawansu ya kai 152 sun isa gida, kawanaki kadan bayan dawowar wasu 242.
Wallafawa ranar:
Tun bayan alkawarin da shugaban kasar Muhammadu Buhari ya yi, na kwashe baki dayan ‘yan Najeriya da suka makale a Libya, aka matsa kaimin tabbatar da kwaso 'yan kasar daga kasar ta Libya.
Hakan ya sa zuwa yanzu ‘yan Najeriya da suka makale a Libya dubu 1, 295 ne aka kwashe zuwa gida cikin watan Nuwamba da ya gabata.
Har yanzu duniya na ci gaba da yin alla wadai, da yadda cinikin bayi ya samu gindin zama a Libya, da kuma yadda wasu ‘yan kasar ke cin zarafin bakin-hauren da suka yi yunkurin tsallakawa zuwa nahiyar turai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu