Najeriya
'Yan bindiga sun sace masu hakar ma'adanai a Kaduna
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta tabbatar da sace wasu mutane 16 dake aikin hakar ma’adinai a kusa da kauyen Bogoma dake karamar hukumar Birnin Gwari.
Wallafawa ranar:
Talla
Yakubu Sabo, jami’in yada labaran rundunar dake Jihar Kaduna yace tuni rundunar ta baza jami’an ta domin farautar wadanda suka sace mutanen.
An dai sace ma’aikatan ne a ranar Talata da ta gabata da daddare, a lokacin da suke kan hanyar komawa gida.
Rahotanni sun ce wadanda suka sace mutanen sun tintibi ‘yan uwan su domin biyan kudin fan sa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu