Isa ga babban shafi
Najeriya

2019: Jam'iyyu sun yi barazanar kauracewa yarjejeniyar zaman lafiya

Jam’iyyu 42 a tarayyar Najeriya, sun yi barazanar kauracewa sa hannu kan yarjejeniyar tabbatar da zaman lafiya yayinda ya rage kwanaki kalilan a yi zaben shugaban kasar a ranar Asabar 16 ga watan Fabarairu.

Akwatin kada kuri'a a Najeriya.
Akwatin kada kuri'a a Najeriya. guardian.ng
Talla

Matsayar jam’iyyun na kunshe cikin sanawar da wakilansu suka fitar, da suka hada da shugaban jam’iyyar AA, Kenneth Udeze, shugaban PCP, Anthony Hamarttan da kuma Mashood Shittu na jam’iyyar ANP.

Gamayyar jam’iyyun sun ce muddin ana bukatar hadin kansu wajen kaucewa rikici yayin zaben, ta hanyar sa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, tilas a cika wasu sharudda da suka gindaya.

Wasu daga cikin muhimman sharuddan sun hada da cewa tilas a kafe ko bayyana sakamakon kuri’ar kowane akwatin zabe kafin kaiwa hedikwatar hukumar INEC, sai kuma haramtawa jami’an tsaro kama jagororin ‘yan adawa da sunan tsare su yayin gudanar zabukan.

A ranar Laraba mai zuwa, 13 ga watan Fabarairu, ake sa ran ilahirin jam’iyyun Najeriya za su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, a karkashin jagorancin tsohon shugaban Amurka, Bill Clinton.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.