Majalisar Najeriya ta ware Naira biliyan 10 ga Zamfara
Majalisar Dattawan Najeriya ta tsayar da kudurin ware Naira biliyan 10 daga kasafin kudin 2019 domin kula da mutanen da hare-haren ‘yan bindiga suka shafa a jihar Zamfara.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Majalisar ta dauki matakin ne bayan muhawarar da Sanata Kabiru Garba Marafa na jam’iyyar APC daga jihar Zamfara ya gabatar a ranar Laraba.
Marafa ya bukaci samar da kudaden tallafi domin agaza wa mutanen da rikicin jihar Zamfara ya raba da muhallansu ko kuma ya shafa.
Majalisar ta yi Allah-Wadai da kashe-kashen da ake fama da su a jihar, in da ta jinjina wa ‘yan Najeriya kan yadda suka yi fitar-dango domin nuna goyon bayansu ga al’ummar jihar.
Kazalika Majalisar ta koka kan yadda matsalar tsaro ta tabarbare a wasu sassan Najeriya da suka hada da Kaduna da Katsina da Sokoto da Filato da Benue da Taraba da sauransu.
Gwamnan jihar Zamfara, AbdulAziz Yari, ya ce, akalla mutane dubu 3 da 500 ne suka rasa rayukansu cikin shekaru biyar sakamakon hare-haren ‘yan bindaga a jihar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu