Isa ga babban shafi
Najeriya

Jigawa: Ambaliyar ruwa ta halaka mutane 20, gidaje dubu 50 sun rushe

Hukumar bada agajin gaggawa ta Jigawa dake  arewacin Najeriya, tace yawan mutanen da ambaliyar ruwa ta halaka a jihar ya kai 20, yayinda kuma ta rusa dubban gidaje gami da lalata tarin amfanin gona.

Wani yankin da ambaliyar ruwa ta mamaye a karamar hukumar Jahun dake jihar Jigawa. (An yi amfani da wannan hoto domin misali kawai)
Wani yankin da ambaliyar ruwa ta mamaye a karamar hukumar Jahun dake jihar Jigawa. (An yi amfani da wannan hoto domin misali kawai) Premium Times Nigeria
Talla

Yayin karin bayani ga manema labarai a garin Dutse, sakataren hukumar agajin gaggawar Yusuf Sani Babura, yace ambaliyar ruwan ta shafi kananan hukumomi 17 daga cikin jumilar 27 dake jihar.

Yanzu haka dai dubban jama’ar da iftila’in ya shafa na tsungune a makarantu, masallatai da wasu gidajen jama’ar da suka basu mafakar wucin gadi.

Kididdigar hukumar bada agajin gaggawar ta Jigawa ta nuna cewar akalla gidaje dubu 50 ambaliyar ruwa ta rusa, yayinda kuma ta shafe gonaki masu yawan gaske da suka hada da na, masara, gero, dawa da kuma shinkafa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.