'Yan bindiga sun halaka mutane 32 a sassan Najeriya a makon jiya
Akalla mutane 32 suka mutu sakamakon hare hare dabam dabam daga kungiyoyi masu dauke da makamai a sassa dabam dabam na Najeriya a makon da ya gabata.
Wallafawa ranar:
Nazari da aka yi a kan alkalumman ya nuna cewa an samu raguwa na kasar da kaso 50 idan aka kwatanta da na makon da ya wuce, inda aka kashe mutane 69.Daga cikin mutane 32 da ak kashen a makon da ya gabata, akwai jami’an ‘yan sanda 2 da kuma wani dan majalisar dokokin jihar Kaduna.
Akasin yadda lamarin yake a makonnin da suka wuce, inda akasarin kashe kashen sun auku a arewa masdo yammacin kasar, inda ‘yan bindiga ke cin zalin wadanda ba su jib a ba su gani ba, an fi samun kashe kashen a yankin arewa ta tsakiyar kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu