Kaduna-'Yan bindiga
'Yan bindiga sun kashe mutane 38 a Kaduna
Gwamnatin Jihar Kaduna dake Najeriya ta tabbatar da kai kazamin harin da ya hallaka mutane akalla 38 a wasu kauyukan dake karamar hukumar Giwa, yayin da aka konawa jama’a kayan abincinsu.
Wallafawa ranar:
Talla
Kwamishinan tsaron Jihar Samuel Aruwan yace bayan kashe mutane an kuma kona gidaje da motoci manyan da kanana tare da amfanin gona a kauyukan Kauran Fawa da Marke da Riheya.
Aruwan yace tuni Gwamna Nasir El Rufai ya aike da sakon ta’aziya ga iyalan wadanda harin ya ritsa da su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu