Isa ga babban shafi
Najeriya-'Yan bindiga

'Yan bindiga sun aurar da 13 daga cikin dalibai mata na Birnin Yauri

Watanni 8 bayan da ‘yan bindiga suka yi awon gaba da daliban sakandiren gwamnatin Tarayyar Najeriya ta birnin Yauri a jihar Kebbi, har yanzu ‘yan bindigar suna rike da fiye da 10 daga cikinsu, duk kuwa da biyan kudin fansa da aka yi, da kuma musayar fursunoni da aka yi a lokuta dabam dabam.

'Yan bindiga sun addabi arewa maso yammacin Najeriya.
'Yan bindiga sun addabi arewa maso yammacin Najeriya. © dailypost
Talla

Wani bincike da jaridar ‘Daily Trust’ da ake wallafawa a Najerya ta gudanar na nuni da cewa an aurar da kimanin dalibai  mata 13 ga ‘yan bindiga, kuma yanzu haka wasu daga cikinsu na da juna biyu.

A ranar 17 ga watan Yunin shekarar da ta gabata ne barayin dajin da ke biyayya ga kasurgumin dan bindigar nan, Dogo Gide  suka afka wa makarantar sakandiren Birnin Yauri a jihar Kebbi, inda suka yi awon gaba da gwamman dalibai da malamai 5.

Binciken da jaridar ‘Daily Trust’ ta gudanar ya nuna cewa tsakanin dalibai 11 zuwa 14 na hannun ‘yan bindigar, kuma daya ne kawai namiji daga cikinsu.

Wasu majiyoyi sun ce tabbas Dogo Gide ya aiwatar da barazanar da ya yi ta aurar da ‘yan matan da suka rage a hannunsa, inda yanzu haka wasu daga cikinsu na da juna biyu.

Wani wanda aka gudanar da tattaunawar sako daliban Yaurin da shi, ya shaida wa jaridar ‘Daily Trust’ cewa  ko a tsakiyar watan Janairu an saki wasu ‘yan mata 3, amma da juna biyu suka dawo gun iyayensu.

Har yanzu gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce tana iya kokarinta na ganin an kubutar da daliban da suka saura a hannun ‘yan bindiga.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.