Isa ga babban shafi

Adadin Mutanen da suka mutu a Fashewar Kano ya kai 9

Adadin wadanda suka mutu sakamakon fashewar da ta afku a Sabon Gari a karamar hukumar Fagge ta jihar Kano da safiyar Talata, ya karu zuwa tara, kamar yadda Ma'aikatar Agaji ta gwamnatin Tarayya ta sanar a wani sako da ta wallafa a shafinta na Twitter.

Masu aikin agaji wajen da aka samu fashewar tukunyar gas a birnin Kano
Masu aikin agaji wajen da aka samu fashewar tukunyar gas a birnin Kano © Abubakar isa Dandago
Talla

Da farko dai Gwamnatin Jihar Kano ta tabbatar da samun fashewar wani abu mai kara a unguwar Sabon Gari amma tace hadarin bai shafi makarantar dake kusa da wurin ba, yayin da rahotanni suka ce mutane 3 suka mutu sakamakon hadarin.

Sanarwar da Kwamishinan yada labarai Muhammad Garba ya gabatarwa manema larabai tace an samu fashewar ce a wani shagon sayar da abincin Kaji dake daura da makarantar dake titin Aba Road a unguwar Sabon Gari dake karamar hukumar Fagge.

Jami'an kungiyar Red Cross da ma'aikatan agaji a wurin da aka samu fashewar tukunyar gas dake Kano
Jami'an kungiyar Red Cross da ma'aikatan agaji a wurin da aka samu fashewar tukunyar gas dake Kano © Abubakar isa Dandago

Kwamishinan yace yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike domin tantance abinda ya haddasa hadarin da illar da yayi, an bukaci mazauna yankin da su kwantar da hankalin su da kuma baiwa gwamnati da jami’an tsaro damar gudanar da ayyukan su.

Shaidun gani da ido sun ce akalla mutane 3 suka mutu sakamakon hadarin, yayin da wasu kuma suka samu raunuka.

Wikilin RFI Hausa

Wakilinmu RFI Hausa a Kano Abubakar Isa Dandago ya ji ta bakin shugaban Yan kasuwar Sabon Gari wanda ya tabbatar masa da samun fashewar, yayin da jami'an aikin agaji ke aiki domin taimakawa wadanda hadarin ya ritsa da su.

Rundunar sojin saman Najeriya ta soke bikin da ta shirya gudanarwa a Kano saboda hadarin da aka samu, yayin da jami'an tsaro suka yi harbi sama domin tarwatsa bata gari dake kokarin amfani da hadarin da aka samu domin satar kayan jama'a.

Kuna iya latsa alamar sauti domin sauraron rahoton Abubakar Isa Dandago.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.