Isa ga babban shafi

Najeriya: 'Yan bindiga sun kashe wani basarake a Kano

An bindige mai unguwar kauyen Maigari a karamar hukumar Rimin Gado ta jihar Kano  a Najeriya,  Dahiru Abba har lahira.

Wata bindiga mai daukar alburusai 50.
Wata bindiga mai daukar alburusai 50. AFP - STEFAN HEUNIS
Talla

Dansa, wanda shine  shugaban karamar hukumar ta Rimin Gadon, Barrister Munir Dahiru Maigari,  ne ya tabbbatar da aukuwa lamarin ga jaridar ‘Daily Trust’ da ake wallafawa a Najeriya.

Ya ce lamarin  ya auku ne da misalign karfe 2 na dare, kuma har an yi masa jana’iza da safiyar  Lahadin nan.

Ya kara da cewa ‘yan bindigar sun kutsa gidan basaraken da karfin tuwo, inda suka ci mutuncinsa kafin su bude masa wuta.

Da aka tuntube shi, kakakin rundunar ‘yan sandan ljihar Kano, SP Abdulllahi Haruna Kiyawa ya ce ba shi da masaniya a game da lamarin, amma zai bincika.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.