Nakiyoyin da 'yan ta'adda ke binnewa sun kashe mutane da dama a Borno
Matafiya da ke tashi daga jihar Borno a arewacin Najeriya zuwa kasashe makota da suka hada da Chadi da Kamaru, sun shiga yanayi na fargaba sakamakon yadda nakiyoyi da aka kyautata zaton cewa mayakan Boko Haram ne suka dasa su tarwatsewa tare da kashe jama’a.
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:22
Cikin rahoton da wakilinmu Bilyaminu Yusu ya aiko mana daga Maiduguri, za a ji cewar fargabar nakiyoyin da ake binnewa kan manyan hanyoyin ta fara barazanar kassara hada-hadar kasuwanci tsakanin jihar ta Borno da kasashen da suka yi iyaka da Najeriya.
Sai a latsa alalmar sautin da ke sama domin sauraron rahoton..
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu