Isa ga babban shafi

Rundunar sojin Najeriya ta fara farautar wadanda ake zargi da daukar nauyin ta'addanci a kasar

Hedkwatar Tsaron Nijeriya ta fitar da sunayen mutum 97 waɗanda ta ce tana nema ruwa-a-jallo kan zarginsu da ayyukan ta'addanci da tsattsauran ra’ayi da kuma barazana ga tsaron kasar.

Wasu dakarun Najeriya a babban sansanin sojin kasar dake Jaji a jihar Kaduna.
Wasu dakarun Najeriya a babban sansanin sojin kasar dake Jaji a jihar Kaduna. AP - AP Photo
Talla

 

Daga cikin wadanda ake nema Kudu Maso Gabashin Nijeriya akwai jagoran dayan reshen kungiyar IPOB Simon Ekpa.

Hedkwatar Tsaron Nijeriya ta sanar da cewa tana neman mutum 97 ruwa-a-jallo kan zarginsu da ta’addanci da tsattsauran ra’ayi da kuma barazana ga tsaron kasar.

Manjo Janar Edward Buba wanda shi ne daraktan watsa labarai na hedikwatar tsaron ne ya bayyana haka a ranar Juma’a a Abuja.

Mutanen da ake nema sun kunshi ƴan ta’adda da kwamandojinsu daga Arewa Maso Gabas da Arewa Maso Yamma da Arewa Maso Tsakiya da Kudu Maso Gabashin Nijeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.