'Yan bindiga sun tsananta hare-hare a Sokoton Najeriya
Rahotanni daga karamar Isa da ke jihar Sokoto a arewa maso yammacin Najeriya, na cewa 'yan bindiga sun dawo da danyen aikinsu na kisan wadanda suka gaza biyan haraji.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kunna - 02:45
Kauyen Gidan Sake na daga cikin kauyukan da suka fuskanci hare-haren 'yan bindigar a baya-bayan nan, inda suka aukawa mutane da daren ranar Laraba, inda suka kashe mutum hudu tare da kona gidaje da ababen hawa.
A cewar mazauna kauyen da ke zaman mafaka a sansanin 'yan gudun hijira na Isa, maharan sun kuma yi awun gaba da mata tara a kauyen Adamawa.
Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken rahoton Faruk Muhammad Yabo.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu