Isa ga babban shafi
nijar

Za a je zagaye na biyu a zaben Nijar

Sakamakon zaben Nijar ya nuna sai an je zagaye na biyu tsakanin Shugaba mai ci Mahamadou Issoufou da babban mai adawa da shi Hama Amadou, saboda rashin samun wanda ya samu kuri'in da ake bukata domin lashe zaben a zagaye na farko.

Hama Amadou da Mahamadou Issoufou za su kara a zagaye na biyu a zaben Nijar
Hama Amadou da Mahamadou Issoufou za su kara a zagaye na biyu a zaben Nijar REUTERS/Joe Penney
Talla

Shugaba Issoufou ne ya ja ragama a zagayen farko na zaben wanda aka gudanar a ranar 21 da 21 na wannan watan na Fabarairu.

Issoufou mai shekaru 63 ya samu kashi 48.41 cikin 100 a zagayen farko yayin da ya ke neman wa’adi na biyu domin ci gaba da zama akan karagar mulki.

Shi kuwa  Hama Amadou, tsohon firaministan kasar wanda kuma aka tsare tun shekarar bara sakamakon zargin sa da safarar yara kanana, ya samu kashi 17.41 cikin 100 a zagayen farko yayin da zai sake karawa da Issoufou a cikin watan Maris mai zuwa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.