Isa ga babban shafi
Nijar

Hukumomin Nijar sun musanta an kai hari kan jami'an agaji

Hukumomin jihar Diffa a Jamhuriyar Nijar, sun karyata jita jita dake nuna cewa ‘yan bidinga na kai hari kan ayarin motocin kungiyoyin agaji dake taimakawa ‘yan gudun hijira da abinci.

'Yan gudun hijira a sansanin Gagamari da ke yankin Diffa a Jamhuriyar Nijar
'Yan gudun hijira a sansanin Gagamari da ke yankin Diffa a Jamhuriyar Nijar
Talla

Fugu Bukar Kantoman Diffa, ya ce a ko da yaushe suna tare da ’yan gudun hijira da kuma jami’an da ke basu agaji, dan haka basu da masaniya a kan labarin.

A cewar Bukar, hasalima tun a farkon fara gudanar da ayyukan agajin, ba’a taba samun wani abu da yayi kama da kaiwa motocin kungiyoyin agaji da ke taimakawa ‘yan gudun hijirar hari ba, dan haka babu kamshin gaskiya cikin labarin.

A halin yanzu kuma Kantoman ya ce, akwai isasshen abinci da aka tanada domin ‘yan gudun hijirar, wanda hakan yasa hatta matsalar karancin abinci ma bata fuskantar su.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.