Isa ga babban shafi

Masu juyin mulkin Nijar sun zargi Faransa da shirin amfani da karfi a kansu

Sojojin da suka yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar sun zargi gwamnatin Faransa da yunkurin amfani da karfin tuwo da wajen mayar da hambararren shugaban kasar Bazoum Muhammed Kan karagar Mulki. 

Janar Omar Tchiani dai ya kasance mai kula da masu gadin fadar shugaban kasa tun a shekara ta 2015 kuma ya kasance na hannun damar tsohon shugaban kasar Issoufou.
Janar Omar Tchiani dai ya kasance mai kula da masu gadin fadar shugaban kasa tun a shekara ta 2015 kuma ya kasance na hannun damar tsohon shugaban kasar Issoufou. © ActuNiger
Talla

 

Ta cikin wata sanarwa da sojojin suka fitar sun ce akwai wasu sojojin wata kasar waje da  ba su fito karara sun kama suna ba, wadanda suka ce sun rika jefa wa masu zanga-zangar goyon bayan sojojin barkonon tsohuwa a Lahadi. 

Sojojin sun kuma zargi Faransa da hada kai da wasu yan Nijar din wajen kitsa yadda za’a  yi amfani da karfin soja wajen afka musu. 

Zanga-zangar ta ranar Lahadi dai ta juye zuwa  tarzoma, inda ta yi sanadin jikkatar mutane 6 da yanzu haka ke kwance a Asibiti. 

Wannan na zuwa ne bayan da Faransa ta yi barazanar cewa duk zanga-zangar goyon baya ko kuma adawa da sojojin kar ta kai kan kadarorinta, ko kuma ‘yan kasarta da ke zaune a Nijar, matukar ba haka ba kuma za su dandana kudarsu. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.