Jami’an 'Yan Sanda 497 aka kashe lokacin da suke gudanar da ayyukan a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:40
Wani rahotan bincike da aka gudanar a Najeriya ya bayyana cewar jami’an Yan Sanda 497 aka kashe lokacin da suke gudanar da ayyukan su a cikin shekaru 6 da suka gabata.
Rahotan da kungiyar SBMorgan dake sanya ido kan harkokin tsaro ta wallafa yace an kuma kashe akalla fararen hula 1,175 a hare haren da aka gani a sassan kasar daga ranar 7 ga watan Janairun shekarar 2015 zuwa 22 ga watan Maris na wannan shekarar.
Dangane da wannan batu Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Tsohon Sufeto Janar na Yan Sandan kasar Alhaji Suleiman Abba, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu