Tattaunawa da Farfesa Mohd Usman kan sabon juyin mulkin Soji a Mali
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:20
Majalisar Dinkin Duniya da Kungiyar Tarayyar Turai da Kungiyar Kasashen Afrika da ECOWAS da wasu manyan kasashen duniya da suka hada da Faransa da Birtaniya da Amurka sun yi tur da juyin mulkin da sojoji suka yi wa gwamnatin rikon kwarya a Mali, inda suka tsare shugaba Bah Ndaw da Firaministansa Moctar Ouane a barikinsu.
A baya-bayan nan shugaban Faransa ya yi barazanar cewa, Kungiyar EU za ta lafta takunkumai ga Mali muddin lamura suka yi sauyawa a kasar.
A game da wannan juyin mulkin, Abdurrahman Gambo Ahmad ya zanta da Farfesa Mohd Usman, shugaban Cibiyar Horas da ‘Yan Majalisar Afrika wanda ya ce, Faransa ce kadai za ta iya maido da zaman lafiya a Mali.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu