Alhaji Muhammadu Magaji gameda dokar tabaci kan karancin abinci a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:45
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya kaddamar da dokar ta baci akan samar da abinci domin shawo kan karancinsa da kuma tsadarsa a kasuwannin kasar. Daga cikin manufofin sabuwar gwamnatin kasar akwai gaggauta gabatarwa manoma takin zamani da raba hatsin da aka tanada a rumbunan gwamnati da baiwa ma’aikatar noma da ta samar da ruwa umurnin hada kai wajen bunkasa noma a lokacin rani da damina da kuma raba sabbin filayen noma har kadada dubu 500 ga matasa domin yin noman.
Domin sanin tasirin wannan shiri, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sakataren tsare tsare na kungiyar manoman Najeriya, Alhaji Muhammadu Magaji, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.....
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu