Yadda jihar Neja ta rabawa mata tukwanen iskar gas don saukaka musu yin girki
Wallafawa ranar:
Kunna - 09:59
Gwamnatin Najeriya ta bayyana fara rabawa mata tukwanen girki na iskar gas, domin sawwaka musu wurin yin girki tare da raba su da amfani da makamashi mai gubarata muhalli. A kokarin da take na kawo karshen dabi’ar sare itatuwa ba bisa ka'ida ba domin samun itatuwan girki, wanda kan haifar da kalubale marar misaltuwa.
Yin amfani da gawayi ko itace wajen girki ba sabon zance bane, toh saidai bayaga haifar da hayaki dake gurbata muhalli ya na kuma shafar lafiya.
Da haka gwamnatin Tarayyar Najeriya ta raba tukanen guda 3300 ga mata marasa karfi a jihar Neja, wadanda aka zakulo daga fadin kananan hukumomi 25 da ke jihar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu