2022, shekara ce da ta zo wa nahiyar Afrika da kalubalen tsaro, tattalin arziki da kuma uwa-uba kalubalen yanayi, sai dai kuma duk da haka akwai nasarori nan da can da aka samu a nahiyar a bara. RFI Hausa ya waiwayi kadan daga cikin muhimman abubuwan da suka wakana a Afrikar.
A ranar 30 ga watan Satumban 2022, jama’ar Burkina Faso suka wayi gari da juyin mulkin da ya hambarar da gwamnatin shugaba Sandaogo Henri Damiba.
Matashi mai shekaru 35 kuma mai rike da mukamin Kyaftin din soja Ibrahim Traore ne ya yi kukan kura tare da hanbarar da gwamnatin, yana zargin gwamnatin shugaba Damiba, wanda shi ma juyin mulki ya yi wa Marc Christian Kabore da zama ‘yar amshin shata, wadda ta kasa tabuka komai game da yanayin tsaron kasar da ta ce dalilin sa ne ya sa ta yi juyin mulkin.
Kuna iya latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin na musamman tare da Rukayya Abba Kabara
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu