Siyasa
Shiri mai farin jini dake leka gidan kowa, dangane da siyasar duniya da irin wainar da ake toyawa akasashen. Bada dama ga Shugabanni da talakawansu su fadi abubuwan da ke gudana a yankunansu. Muna kawo shirin a ranar Laraba da safe da maimaicinsa Alhamis da yamma.
Ci gaban karatuSaurari kashin karshe
Daukacin kashi-kashi
-
Najeriya ta ayyana shiga matsalar tattalin arziki a hukumance
A satin da ya gabat gwamnatin Najeriya ta ayyana shiga matsalar tattalin arziki da kasar ta yi a hukumance; shirin kuma ya tabo batun dakon sakayyar da gwamnatin Jamhuriyyar Nijar zata yiwa babbar Jam'iyyar adawar kasar da ta narke cikinta don mara mata baya.04/09/201620:34 -
Najeriya ta sanar da lalacewar tattalin arziki
Cikin shirin Dandalin Siyasa na wannan mako Abdulkarim Ibrahim Shikal ya tabo batun lalacewar tattalin arzikin Najeriya da kuma dambarwar siyasar kasar Nijar.03/09/201620:34 -
Sauke Masarautun gargajiya a Bauchi
A cikin shirin wannan makon tare da Abdulkarim Shikkal, ya duba matakin da gwamnati Bauchi mai ci ta dauka na sauke nadin sarakunan gargajiya da gwamnatin da ta shude ta yi da kuma sabbin rigingimun siyasa dake kunon kai a jihar.28/08/201619:40 -
Soke Masarautu 1000 ya bar baya da kura a Jihar Bauchi
Shirin ya tabo batun daukar matakin soke wasu manya da kuma kananan masarautu har 1000 da tsohuwar gwamnatin jihar ta kafa, da Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta dauka.27/08/201619:40 -
Ko Jamiyyar Adawa za ta hade da Jamiyyar da ke Mulki a Janhuriyar Nijar?
Cikin shirin namu na Dandalin Siyasa Abdolkarim Ibrahim Shikal ya duba batun shigar 'yan adawa cikin Gwamnatin kasar Nijar.20/08/201620:30 -
Rikicin Majalisar Wakilan Najeriya
Shirin dandalin Siyasa ya duba jawaban Shugaban kasar Nijar Mohammadu Issofou yayin bukukuwan samun yanci kai a kasar da kuma rikicin Majalisar Wakilan Najeriya sakamakon badakalar kasafin kudin shekarar 2016, tare da Abdulkarim Ibrahim Shikkal.07/08/201620:10 -
Dandalin siyasa na yau asabar zai yo dubi kan batun yiwa kudin Jamhuriyar Nijar gyara
A cikin shirin dandalin siyasa Abdoulkarim Ibrahim ya ji ta bakin wasu daga cikin yan Majlisun Jamhuriyar Nijar dangane da batun yiwa kudin tsarin mulkin kasar gyara.Rikici ya kaure tsakanin yan Najeriya da Nijar a yankin Damagaram dangane da batun wuraren noma.04/06/201621:06 -
Ya dace Shugaba Buhari ya saurari koken yan kasar
A cikin shirin dandalin siyasa Awwal Ahmad Janyau ya duba yanayin siyasar cire tallafin mai fetur.A yi saurare lafiya.14/05/201620:32 -
Siyasar Najeriya da sauren kasashen Afrika
A cikin shirin Dandalin siyasa Abdoulkarim Ibrahim yayo dubi dangane da batutuwan siyasa a Najeriya ,Nijar dama Chadi,kasar da hukumar zabe ta sanar da cewa Shugaba Idriss Deby Itno ne ya lashe zaben kasar na ranar 10 ga watan Afrilu.23/04/201619:59 -
Ana kammala zabubukan jamhuriyar Nijar
An kammala zaben shugaban kasa da na 'yan majalisar dokoki a jamhuriyar Nijar, inda bayan nasarar da shugaban kasar Issoufou Mahamadou ya yi nasarar lashe zaben, haka zalika jam'iyyarsa ta PNDS Tarayya ta samu kujeru 75 daga cikin 171 da ake da su a zauren majalisar kasar.Tuni dai aka kaddamar da sabuwar majalisar dokokin kasar, to sai dai zabubukan sun bar baya da kura, kamar dai yadda za a ji a wannan shiri na Dandalin Siyasa tare da Garba Aliyu Zaria.26/03/201619:37 -
'Yan adawa ba za su shiga zagaye na biyu na zaben Nijar ba
Kawancen jam'iyyun adawa na COPA a Jamhuriyar Nijar ya ce dan takararsu Hama Amadou ba zai shiga zagaye na biyu na zaben shugabancin kasar da za a yi a ranar 20 ga watan maris ba, inda za a fafata tsakanin Hama Amadou da kuma shugaba mai ci Issoufou Mahamadou.To sai dai jam'iyyar Moden Lumana Africa wadda ta tsayar da Hama a wannan zabe, ta ce ba gaskiya ba ne, dan takararta bai janye daga zaben ba, sai dai suna adawa da yadda aka tsara gudanar da shi.Shirin Dandalin Siyasa na wannan mako, Garba Aliyu Zaria ya yi dubi ne a game da wannan dabarwa.12/03/201620:01 -
Shirye-shiryen zaben shugaban kasa a Jamhuriyar Nijar
Shirin Dandalin Siyasa na wannan mako, tare da Bashir Ibrahim Idirs, zai mayar da hankali ne a game da shirye-shiryen zaben shugaban kasa da za a yi ranar 21 ga watan fabarairun 2016 a Jamhuriyar Nijar.10/01/201621:07 -
An kama tsohon shugaban Majalisar Dokokin Nijar Hama Amadou
A daidai lokacin da ake shirye-shiryen zaben shugaban kasa na 'yan Majalisa a watan fabarairun 2016, hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun cafke tsohon shugaban Majalisar Dokokin kasar Hama Amadou wanda ake zargi da fataucin jarirai daga Najeriya, yayin da a jihar Kebbi da ke Tarayyar Najeriya, jam'iyyar PDP ke neman a tube gwamna Atiku Bagudu, saboda a cewar jam'iyyar, gwamnan mai laifi ne kafin zaben sa.Wadannan batutuwa ne shirin na wannan mako ya mayar da hankali a kai tare da Bashir Ibrahim Idris.22/11/201520:00 -
An tantance ministoci a Najeriya, yayin da ake shirye shiryen zaben shugaban kasa a Nijar
An kammala aikin tantance wadanda shugaban Najeriya ke son nadawa a matsayin ministoci, yayin da a Jamhuriyar Nijar jam'iyyun siyasa suka daura damara domin zabubukan da za a yi a kasar cikin watan fabarairu mai zuwa. Wadannan batutuwa ne Bashir Ibrahim Idris ya duba a cikin shirin Dandalin Siyasa na wannan mako.01/11/201521:00 -
Zaben kasar Cote D'ivoire
A kasar Cote d'Ivoire a ranar 25 ga watan Oktoban nan ne za a gudanar da zaben shugabancin kasar,Bashir Ibrahim Idris ya dubo mana halin da ake ciki a wannan shiri na siyasa.24/10/201520:22
Siyasa
Shiri mai farin jini dake leka gidan kowa, dangane da siyasar duniya da irin wainar da ake toyawa akasashen. Bada dama ga Shugabanni da talakawansu su fadi abubuwan da ke gudana a yankunansu. Muna kawo shirin a ranar Laraba da safe da maimaicinsa Alhamis da yamma.