Siyasa
Shiri mai farin jini dake leka gidan kowa, dangane da siyasar duniya da irin wainar da ake toyawa akasashen. Bada dama ga Shugabanni da talakawansu su fadi abubuwan da ke gudana a yankunansu. Muna kawo shirin a ranar Laraba da safe da maimaicinsa Alhamis da yamma.
Ci gaban karatuSaurari kashin karshe
Daukacin kashi-kashi
-
Dambarwar APC kan shugabancin Majalisar Najeriya
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim ya yi nazari ne kan dambarwar shugabancin Majalisar Tarayyar Najeriya, in da wasu 'ya'yan jam'iyyar APC mai mulki ke zargin jagoran jam'iyyar na kasa, Bola Ahmed Tinubu da kokarin mamaye Majalisar domin bukatun kansa a shekarar 2023.24/04/201910:26 -
Yanayin siyasar Najeriya bayan dage zaben zuwa ranar 23
Bayan sanar da dage zaben Shugaban Najeriya zuwa ranar 23 ga watan Fabrairu daga hukumar zaben kasar ta INEC,yan kasar na ci gaba da bayyana tsokacin su a kai,yayinda yan siyasa ke zargin junan su da shirya magudi, a yau Laraba jam’iyya ta APC mai mulkin Najeriya tayi watsi da zargin dan takarar Jam’iyyar PDP Atiku Abubakar da cewar shugaban kasa Muhammadu Buhari na yiwa dimokiradiya zagon kasa wajen mulkin kama karya.Bashir Ibrahim Idris a cikin shirin Dandalin siyasa ya mayar da hankali zuwa ga batun zaben na Najeriya.20/02/201910:25 -
Yakin zaben Najeriya,hasashen jama'a a wasu yankunan kasar
A cikin shirin dandalin siyasa,Bashir Ibrahim Idris ya mayar da hankali zuwa ra'ayin wasu daga cikin yan Najeriya dangane da yanayin siyasar kasar da kuma hasashen su zuwa yan takara a zaben.23/01/201903:43 -
Labarun Afrika na shekara 2018
Shekara ta 2018 ta kasance shekara dake tattare da kalubale ga Nahiyar Afrika,kama da zabe,kiwon lafiya,siyasa,tattalin arziki ,yanayi.A cikin shiri na musaman,Ahmed Abba ya yo bitar wasu daga cikin muhiman labaren Afrika tareda mayar da hankali zuwa kasashen yankin.02/01/201920:34 -
Jamhuriyar Nijar a shekara ta 2018
Shekara ta 2018 ta kasance wadda abubuwa da dama suka gudana a Jamhuriyar Nijar, kama daga siyasa, tattalin arziki, tsaro.A cikin shirin Abdoulaye Issa ya yi bitar wasu daga cikin manyen batutuwa da suka auku a Jamhuriyar Nijar.01/01/201920:54 -
Shugaban Najeriya a Jamhuriya ta biyu, Alhaji Shehu Usman Shagari ya rasu
A cikin shirin karshen shekara na 2018,Garba Aliyu Zaria ya mayar da hankali zuwa labaren Najeriya,ta fuskar siyasa,tattalin arziki,kiwon lafiya da kuma zamantakewa.Garba Aliyu Zaria ya duba zancen rasuwar Alhaji Shehu Shagari wanda shi ne Turakin Sokoto da ya yi mulkin Najeriya tsakanin shekara ta 1979 zuwa 1983.Ya mutu yana da shekaru 93 bayan rashin lafiya a babban Asibitin Abuja.01/01/201920:06 -
An fara yakin neman zabe a Najeriya
A cikin shirin Siyasa ,Bashir Ibrahim Idris ya mayar da hankali zuwa siyasar Najeriya,musamman soma yakin neman zabe da aka fara a kasar.Da dama daga cikin yan kasar sun mayar da hankali zuwa manyan ayuka da kowane daga cikin yan takara ke daukar alkawalin gudanarwa bayan zabe.Shirin siyasa daga sashen hausa na rediyo Faransa RFI.21/11/201810:55 -
Waiwaye kan muhimman batutuwan siyasar Najeriya da suka fi daukar hankali
Shirin dandalin Siyasa yayi waiwaye wanda masu iya magana suka ce adon tafiya kan bututuwan siyasa da suka fi daukar hankali a tarayyar Najeriya, tare lekawa Jamhuriyyar Nijar dan jin wainar da ake toyawa a fagen siyasar kasar.01/01/201720:20 -
ECOWAS ta bukaci Jammeh ya mika mulki
Shirin dandalin siyasa na wannan makon tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya tattauna ne kan rikicin siyasar Gambia, in da shugaba mai ci Yahya Jammeh ya ki amincewa da miki mulki duk da kashin da ya sha a zaben shugabancin kasar da aka gudanar a farkon watan Disamba. Kazalika shirin ya tattauna kan kudirin kasafin kudin shekara mai zuwa da shugaba Muhammadu Buhari ya gabatar wa zaman hadin gwiwa na majalisar tarayyar Najeriya17/12/201621:05 -
Jam'iyyar adawa ta lashe zaben Ghana
Shirin dandalin siyasa na wanna makon tare da Abdulkarim Ibrahim Shikal ya tattauna ne kan nasarar da Nana Akuffo-Addo ya samu a zaben shugabancin kasar Ghana bayan ya doke shugaba mai ci John Dramani Mahama. Har ila yau shirin ya zanta kan zaben Gambia, in da shugaba Yahaya Jammeh ya yi amai ya lashe dangane da amincewa da sakamakon zaben10/12/201620:15 -
Zaben fidda gwani na jam'iyyar Republican a Faransa
Shirin Siyasa a wannan makon ya mayar da hankali kan zaben fidda gwani da jam'iyyar Republican a Faransa ta shirya don tsayar da dan takara.28/11/201620:04 -
Siyasar rikicin Libya
Cikin shirin namu na Dandalin Siyasa Awwal Janyau ya duba cika shekaru biyar da mutuwar Marigayi Muammar Gaddafi.22/10/201620:20 -
Dandalin Siyasa
Cikin shirin na mu na Dandalin siyasa na wannan lokaci wanda Garba Aliyu Zaria ya shirya zamu ji ziyarar da wasu tsoffin Gwamnoni karkashin jagorancin tsohon Gwamnan jihar Neja Babangida Aliyu suka kai don yiwa al'ummar arewa maso gabas jaje na halin da suka shiga na bala'in kungiyar Boko Haram.24/09/201620:12 -
Dandalin Siyasa
Cikin wannan shiri za'aji cewa Shugaban Ghana John Dramani Mahama da sauran 'yan takaran shugabancin kasar sun yaki takardun neman shiga zabe daga Hukumar Zabe a Accra Ghana.Garba Aliyu Zaria na dauke da shirin.17/09/201619:57 -
Dandalin Siyasa
Cikin wannan shiri na Dandalin Siyasa Garba Aliyu Zaria ya tabo siyasar Kano tsakanin Gandujiya da Kwankwasiya.10/09/201620:12
Siyasa
Shiri mai farin jini dake leka gidan kowa, dangane da siyasar duniya da irin wainar da ake toyawa akasashen. Bada dama ga Shugabanni da talakawansu su fadi abubuwan da ke gudana a yankunansu. Muna kawo shirin a ranar Laraba da safe da maimaicinsa Alhamis da yamma.