Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyi kan wadatar sabbin kudaden Naira a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 15:25
Shirin Ra'ayoyin Masu Saurare na wannan rana ya tattauna ne gaame da yadda babban bankin Najeriya CBN ya zargi bankunan kasuwanci na kasar da kin bai wa jama’a sabbin kudaden Naira don janye tsoffi kamar dai yadda aka shata nan zuwa ranar 31 ga wannan wata na janairu.
Talla
Yayin da CBN ya bukaci jama’a da su daina karbar tsoffin kudade a cikin bankuna, wasu kuwa na zargin jami’an bankuna da karbar na goro ne kafin su amince su canza wa mutane tsoffin kudaden.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu