Isa ga babban shafi
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Kan tayin da Aljeriya ta gabatarwa gwamnatin sojin Nijar

Wallafawa ranar:

A daidai lokacin da aka gaza tattaunawa tsakanin sojojin da suka kwaci mulki a Jamhuriya Nijar da kuma kungiyar Ecowas, a nata bangare Aljeriya, ta ce ta samu wasikar amincewa da tayin shiga tsakanin da kasar wadda ke Arewacin Afirka ta gabatar wa gwamnatin sojin.  

Jami'an tsaron Nijar kenan da ke gudanar da aikin sintiri a Yamai, babban birnin kasar ranar 23 ga Agusta, 2023.
Jami'an tsaron Nijar kenan da ke gudanar da aikin sintiri a Yamai, babban birnin kasar ranar 23 ga Agusta, 2023. AFP - -
Talla

Kimanin makonni 5 da suka gabata ne Aljeriya ta ce tana goyon bayan kafa gwamnatin rikon kwarya da za ta share watanni 6 kafin shirya zabuka a Nijar.  

Duk da yake ba su ce za su yarda a gudanar da zabe cikin watanni 6 masu zuwa ba, amma sojojin sun amince Aljeriya ta shiga tsakani a wannan takaddama.  

Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin da Nasiru Sani ya gabatar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.