Rawar da kasashen Afrika suka taka a wasannin Olympic a birnin Tokyo na Japan
Wallafawa ranar:
Kunna - 10:07
Kimanin makwanni biyu kenan da aka kammala wasannin Olympic na Tokyo 2020, inda kasashen duniya 205 da kuma ‘yan wasa fiye da dubu 11 suka barje gumi a mabanbantan wasanni.
Amurka da China da Japan da Birtaniya da Rasha ke kan gaba wajen samun lambobin yabo na zinari da azurfa da kuma Tagulla, yayin da kasashen Afrika aka yi musu fintinkau, in ban da ma Kenya wadda ta fi taka rawar gani a nahiyar Afrika, domin kuwa ta lashe zinari 4 da azurfa hudu da tagulla biyu kuma ita ce ta farko a nahiyar amma ta 19 a duniya.
To ko me masana lamurra wasanni za su ce game da rawar da Kasashen Afrika suka taka a gasar?
Wani abun da ake ganin tamkar abin kunya ne shi ne yadda ‘yan wasan Najeriya suka gudanar da zanga-zanga a can birnin na Tokyo saboda wasu dalilai da suka hada da haramta ma wasunsu fafatawa saboda ta’amulli da kwayoyi kamar yadda gwaji ya nuna, yayin da kamfanin Puma ya soke yarjejeniyar Dala miliyan 2.7 da ke tsakaninsa da Najeriya saboda abubuwan da suka wakana a Tokyon.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu