Isa ga babban shafi

'Yan takara 10 ne za su kara a zaben shugaban kasa a Chadi

‘Yan takara goma ne za su kara da juna a zaben shugabancin kasar Chadi da za a gudanar ranar 6 ga watan Mayu mai zuwa, da suka hada maza 9 da kuma mace daya.

Taswirar kasar Chadi.
Taswirar kasar Chadi. CGTN Africa
Talla

Ten candidates to run for May 6 presidential elections

 

Daya daga cikin wadanda za su tsaya takarar akwai Mahamat Idriss Déby da aka fi sani da Kaka wanda ke rike mukamin shugaban rikon kwaryar kasar.

Farkon hawansa karagar Mulki dai ya yi alkawarin ba zai tsaya takarar ba, sai gashi sunan sa na cikin wadanda suka tsaya, Janar Deby dai Soja ne da ya samu horo a kasar sa Chadi da kuma Faransa, sannan yana da mata uku da yara masu yawa.

Sai Firaministan sa Succès Masra, ya na daya daga cikin ‘yan takarar, wanda a can baya shi ne babban dan adawa ga gwamnatin sojin kasar.

Sakamakon wannan adawar ta shi ce ta sa aka kore shi daga kasar amma a shekarar da ta gabata Deby ya dawo da shi kuma ya ba shi mukamin firaminista a watan janairun shekarar nan ta 2024.

Sauran ‘yan takarar sun hada da Alladoum Djarma Baltazar, da Théophile Bongoro Bebzouné, da Nasra Djimasngar, da Mansiri Lopsikreo, da Albert Pahimi Padacké, da Yacine Abdramane Sakine  da kuma wata mace guda daya Lydie Beassemda

Kotun kundin tsarin mulkin kasar ta cire sunayen Nassour Ibrahim Neguy Koursum da Rakhis Ahmat Saleh bisa samun su da aikata ba daidai ba.

Yaya Dillo, ya kasance babban dan hamayya ne a kasar kafin sojojin kasar su kashe shi a watan Febrirun shekarar nan a shelkwatar jam’iyyar sa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.