Isa ga babban shafi
Italiya

Ruftawar gini ya kashe mutane biyu a Italiya

Wani gini daya rufta a yankin Sicilia dake kasar Italiya, ya kashe mutane biyu a jiya da daddare. Tun a ranar litinin ‘Yan kwanakwana suka fara sa mutane su kauracewa yankin bayan mazauna yankin sun ce suna jin alamar zubewar gini.  

Firaministan kasar Italiya Mario Monti
Firaministan kasar Italiya Mario Monti REUTERS/Eric Gaillard
Talla

Wadanda suka mutu sun hada da Ignazio Accardi, dan shekaru 85 da Antonino Cina, dan shekaru 54, wadanda duk aka cirosu daga kasan ginin.

Rahotannin sun nuna cewa ana neman wasu mata biyu da ba gansu ba, wadanda aka ce shekaransu ya kai 80 da 74.

Har ila yau dunbin mutane sun samu raunuka a lokacin da ginin ya zube, kamar yadda rahotanni suka tabbatar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.